Buhari zai je duba lafiyarsa a London bayan taron yanayi a Kenya
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya kama hanyar zuwa birnin London don duba lafiyarsa. balaguron da zai dauke shi tsawon makwanni 2.
Wallafawa ranar:
Wata sanarwa dauke da sa hannun kakakin fadar shugaban Najeriya Femi Adesina ta ce shugaba Buhari zai fara yada zango a Kenya wajen taron Majalisar Dinkin Duniya gabanin wucewa Birtaniya.
Ko a watan Maris din 2021 sai da shugaba Muhammadu Buhari ya harzaya London wajen duba lafiyarsa ko da ya ke an dakatar da makamanciyar ziyarar a watan Yunin shekarar.
Sanarwar fadar shugaban na Najeriya, ta ce tawagar shugaba Muhammadu Buhari za ta bar kasar a yau talata tare da rakiyar ministan waje Geoffrey Onyeama dana muhalli Sharon Ikeazor baya ga Babagana Monguno da kuma Ambasada Ahmed Rufa’I Abubakar sai Abike Dabiri-Erewa.
Buhari zai kasance a taron na Majalisar Dinkin Duniya har zuwa ranar 4 ga watan nan inda zai gana da shugaban Kenya Uhuru Kenyatta.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu