Isa ga babban shafi
Najeriya - Katsina

An katse layukan sadarwa a wasu yankunan jihar Katsina

Bayanai daga jihar Katsina a tarayyar Najeriya sun ce an katse layukan wayoyin sadarwa a kananan hukumomi 13 da ke fama da hare-haren ‘yan bindiga.

Manyan turakun kamfanonin sadarwa a Najeriya.
Manyan turakun kamfanonin sadarwa a Najeriya. © Nairametics
Talla

Kananan hukumomin da matakin ya shafa sun hada da Sabuwa, Faskari, Dandume, Batsari, Danmusa, Kankara, Jibia, Safana, Dutsin-Ma da Kurfi, sai kuma  Funtua, Bakori da Malumfashi, wadanda ke kusa da dajin Ruggu inda mafi yawan 'yan bindigar ke buya.

A baya bayan nan ne dai Hukumar kula da Sadarwa ta Najeriya NCC ta musanta shirin rufe layukan sadarwa a jihar Katsina.

A farkon watan Satumban da muke hukumar ta NCC ta baiwa kamfanonin sadarwa umarnin rufe dukkanin layukansu a jihar Zamfara mai makwabtaka Katsina daga ranar 3 ga watan na Satumba, domin baiwa hukumomin tsaro damar gudanar da ayyukan kawo karshen ‘yan bindigar da suka addabi jama’a.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.