'Yan bindiga sun kashe mutane 12 tare da yi wa mata fyade a Katsina
A Najeriya ‘yan bindiga sun kashe mutane 12 tare da raunata da dama a wani harin da suka kai kauyen Duba dake karamar hukumar Batsari ta jihar Katsina.
Wallafawa ranar:
Wani mazaunin garin Batsari da ya nemi a sakaya sunansa ya ce ‘yan bindigar sun afka wa kauyen wanda nisan kilomita kalilan ne tsaninsa da Batsari da yamacin Asabar ne, inda suka yi wa dimbim mata fyade tareda yin awon gaba da dabbobi da dama.
Rahotanni sun ce ‘yan bindigar da suka wa kauyen sun ci Karensu ba babbaka ba tare da fuskantar turjiya ba. Kuma bayan mutane 12 da suka mutu, yanzu ana nan ana neman mutane da suka bace a dazukan kusa da kauyen.
Ya zuwa lokacin hada wannan labari, babu wata hukuma da ta tabbatar da aukuwar lamarin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu