Najeriya: An tsige hakimin Kankara saboda laifin taimaka wa 'yan bindiga
A Najeriya gwamnatin jihar Katsina ta sauke hakimin Kankara, Alhaji Yusuf Lawal saboda samun sa da laifin taimaka wa ‘yan bindiga.
Wallafawa ranar:
A ranar 12 ga watan Disamban shekarar 2020 ne wani kwamandan daji, Auwalun Daudawa, wanda ya gamu da ajalinsa kwanan nan ya sace dalibai sama da 300 a garin Kankara, satar dalibai na farko da wata kungiyar masu aikata laifi ta taba yi, bayan Boko Haram.
Sakataren karamar hukumar, Alhaji Bello Mamman-Ifo, ne ya bada sanarwar, ta bakin jami’ain yada labaran masarautar, Alhaji Ibrahim Bindawa, a Katsina.
Ya ce binciken da suka gudanar a kan zargin da ake wa hakimin kan taimaka wa ‘yan ta’adda ya nuna cewa lallai ya aikata laifin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu