Najeriya-Rashawa
Rashawa za ta hana Najeriya ci gaba - Ganduje
Gwamnan jihar Kano a Najeriya, Abdullahi Umar Ganduje ya ce kasar ba za ta samu ci gaba ba saboda cin hanci da rashawar da ya dabaibaye ta.
Wallafawa ranar:
Talla
Ganduje ya bayyana hakan ne jiya Alhamis yayin kaddamar da wani kwamiti mai mutune takwas kan wasu dabarun yaki da rashawa a jihar.
Gwamnan wanda sakataren gwamnatin jihar Usman Alhaji ya wakilce shi, ya kaddamar da kwamitin ne a da nufin rage cin hanci da kuma tabbatar da gudanar da al'amura a bayyane a fadin jihar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu