Isa ga babban shafi
Najeriya - Zamfara

Gwamnatin Zamfara ta musanta ceto 'Yan matan sakandaren Jangebe

A Najeriya, Gwamnatin jihar Zamfara ta musanta rahotannin ceto ‘yan matan sakandaren Jangebe, inda tace har yanzu tana kan ƙoƙarin ganin an sako ɗaliban sama da 300 da ‘yan bindiga suka sace.

Kabiru Sani Jangebe, mahaifin daya daga cikin dalibai mata na sakandaren Jangebe da 'yan bindiga sukayi garkuwa da su.
Kabiru Sani Jangebe, mahaifin daya daga cikin dalibai mata na sakandaren Jangebe da 'yan bindiga sukayi garkuwa da su. AP - Ibrahim Mansur
Talla

Sanarwar da fadar gwamnatin jihar ta fitar a dazunan ta ƙaryata rahotannin maban-banta da ke cewa an sako ɗaliban.

Tun a tsakiyar daren Juma'a ne ƴan bindigar suka kustsa makarantar sakandaren kwana ta Mata kuma suka yi awon gaba da ɗaliban 317.

Masauda Umar,  daya daga cikin dalibai mata na sakandaren Jangebe da ta buya a karkashin gado lokacin da 'yan bindiga suka shiga makarantar su.
Masauda Umar, daya daga cikin dalibai mata na sakandaren Jangebe da ta buya a karkashin gado lokacin da 'yan bindiga suka shiga makarantar su. AP - Ibrahim Mansur

Majalisar Dinkin Duniya, da gwamnatocin kasashen Amurka da na Birtaniya duk sun bayyana harin da aka kai a makarantar sakandaren 'yan mata da ke Jangebe a matsayin abin ban tsoro tare da yin kira da a sake su ba tare da bata lokaci ba.

Ana samun ra'ayoyi maban-banta kan biyan kudin fansa domin ceto munaten da 'yan bindiga ke garkuwa da su, inda ake cewa shine ummul aba'isin yawaitan lamarin, yayin da wasu ke ganin babu sauran dabara muddun akayi garkuwa da mutane face biyan kudin da kare lafiya da rayuwar wadanda aka sace.

Zubairu Sanusi, daya daga cikin Malami kuma mahaifin 2 daga cikin dalibai mata na sakandaren Jangebe da 'yan bindiga sukayi garkuwa da su.
Zubairu Sanusi, daya daga cikin Malami kuma mahaifin 2 daga cikin dalibai mata na sakandaren Jangebe da 'yan bindiga sukayi garkuwa da su. AP - Ibrahim Mansur
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari  yayin jajantawa iyalen wadanda lamarin ya shafa, yace, ba zai“ ba da kai bori ya hau ba kan barazanar  ‘yan bindiga” da ke jiran “biyan kudin fansa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.