Harin kunar bakin wake ya kashe mutane 3 a Masallacin garin Bama
Wasu yan kunar bakin wake sun kashe mutane 3 a wani Masallaci a garin Bama dake Jahar Borno a Najeriya. Shidai wannan garin yanzu haka ana kan sake gina shi bayan da ‘ya’yan kungiyar Boko Haram suka kacaccala shi a yankin Arewa maso gabashin kasar.
Wallafawa ranar:
Wani ganau, mai suna Baba shehu Gulumba da ke a garin Bama ya ce maharan mace da Namiji, sun tarwatsa kansu ne a lokacin da ake sallar Asubah a garin na Bama da ke jihar Borno.
Babban jami’in Sojin Najeriya da ke aiki a garin na Bama ya shaida wa manema labarai cewar hakika harin ya faru, kuma a lokacin, an kwashe akalla mutane 9 da suka samu raunuka zuwa Assibiti, kuma bayanai na nuna cewar ankaisu ne zuwa Asibiti a garin Maiduguri.
Harin na zuwa ne akalla sati guda bayan da mutanen garin suka fara komawa gida sakamakon zaman lafiya da aka fara samu a yankin.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu