Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojoji sun yi gargadi bayan harin Boko Haram a Borno

Rundunar Sojin Najeriya ta fitar da sanarwar gargadi bayan harin da mayakan Boko Haram suka kai jiya laraba a jihar Borno tare da sace manyan motocinsu da ke makare da makamai.

Babban Hafsan Sojin Najeriya Tukur Yusuf Buratai
Babban Hafsan Sojin Najeriya Tukur Yusuf Buratai thenewsnigeria
Talla

Kamar yadda kamfanin dilancin labaran Faransa, AFP, ya rawaito rundunar ta tura sakon kar-ta-kwana ga dukkanin barikoki da shingayen bincike da ke yankuna arewacin kasar inda abin ya faru domin tsananta bincike.

AFP ya ce an sace motoci 2 na makamai da tankokin yaki 2 lokacin da mayakan suka kai harin ba za ta da yammacin jiya laraba a garin Mainok da ke Borno.

Rahotan ya ce anji karar harbe-harbe lokacin da mayakan ke musayar wuta tsakanin su da sojojin da ke samar da tsaro a Yankin.

Akalla mayakan Boko Haram 9 aka kashe a harin da ke kasance irinsa mai karfi a tsawon makonni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.