'Yan bindiga sun hallaka mutane 6 a Kaduna
Rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, ta tabbatar da mutuwar mutane shida, a wani hari da ‘yan bindiga suka kai a karamar hukumar Jema’a.
Wallafawa ranar:
‘Yan bindigar su kai harin ne a yankin Bakin Kogi da ke masarautar Kanikon da ke karamar hukumar ta Jema’a, inda suka hallaka maza 4 da mata 2, tare da raunata wasu mutanen 4.
Kakakin ‘yan sandan jihar ta Kaduna Aliyu Mukhtar ya ce a halin yanzu, hadin gwiwar sojoji da yan sanda suna kan farautar ‘yan bindigar.
A shekarar da ta gabata Jihar kaduna ta yi fama da hare-haren ‘yan bindiga musamman a yankin Birnin Gwari, dalilin da ya sanya aka girke sojoji da ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro a yankunan da matsalar ta shafa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu