Majalisar Dinkin Duniya ta maido da ayyukanta a Rann
Ofishin bada agajin jinkai na Majalisar Dinkin Duniya OCHA, ya sanar da komawa bakin ayyukansa a garin Rann na jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.
Wallafawa ranar:
Sai dai Ofishin na OCHA ya ce ma’aikatan nasa ba wai zasu rika kwana ba ne a garin na Rann ba, kamar yadda suke a baya, har sai an tabbatar da cikakken tsaro a yankin.
A ranar 2 ga watan Maris, Majalisar Dinkin Duniya ta janye ilahirin jami’anta daga garin na Rann, bayan Farmakin da mayakan Boko Haram suka kai ranar 1 ga watan, inda suka kashe mutane 8 ciki harda jami’an agaji 3 suka kuma sace ma’aikaciya jiyya 1.
Akalla mutane 80,000 jami’an agaji na majalisar Dinkin Duniya dana sauran kungiyoyi suke lura da su a garin na Rann da ke jihar Borno.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu