Sai Buhari ya koma PDP kafin na ba shi shawara- Lamido
Tsohon gwamnan jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido ya ce, sai shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya koma babbar jam’iyyar adawa ta PDP kafin ya ba shi shawarar magance wasu matsalolin da ake fuskanta a gwamnatinsa.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
A yayin zantawa da sashen hausa na rfi, Lamido ya ce, matsalar wawure dukiyar talakawa ta fi kamari a mulkin Buhari idan aka kwatanta da tsohuwar gwamnatin PDP da ta shude.
A cewar Lamido sun tattauna da ‘ya’yan jam’iyyar APC mai mulki da suka tabbatar mu su da irin sace-sacen da ake yi a gwamnatin Buhari.
Kazalika tsohon gwamnan ya alakanta salon mulkin Buhari da damfara, musamman ganin yadda gwamnatin Buharin ta gza magance matsalar tsadar kayayyaki duk da alamun da ta nuna na tinkarar wannan matsalar gabanin samun nasara a zaben 2015.
Cikakkiyar hira da Sule Lamido kan bukatar komawar Buhari PDP
Jam’iyyar PDP da ta rasa mulkii a zaben 2015 na na ci gaba da sasanta magoya bayanta domin ganin ta karbe mulki a zaben 2019.
Tsohon Gwamnan na Jigawa na daya daga cikin masu neman tikitin takarar shugabancin kasar a karkahsin inuwar jam’iyyar PDP a shekara mai zuwa.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu