Isa ga babban shafi
Najeriya

Gwamnatin Borno ta kara tsawaita dokar hana zirga-zirga

Gwamnatin Jihar Borno ta kara tsawaita wa’adin dokar hana zirga-zirga da ta kafa daga karfe 8 na dare zuwa karfe 6 na safe.

Wasu daga cikin jami'an sojin Najeriya a garin Baga da ke wajen birnin Maiduguri. 13 ga watan Mayu, 2013.
Wasu daga cikin jami'an sojin Najeriya a garin Baga da ke wajen birnin Maiduguri. 13 ga watan Mayu, 2013. REUTERS/Tim Cocks
Talla

Kwamishinan yada labaran jihar Dr Muhammad Bulama ne ya bada sanarwar, wadda ta ce an kara wa’adin dokar da tsawon kwanaki bakwai, wato zuwa ranar 20 ga watan Janairu da muke ciki.

Karo na uku kenan da gwamnatin Jihar ta Borno ke kara wa’adin, bisa shawarar rundunar sojin Najeriya.

Sanarwar ta ce, an dauki matakin ne domin bai wa rundunar sojin Najeriya karin lokaci, domin daukar matakai na karasa murkushe duk wata barazanar tsaro da ragowar mayakan kungiyar Boko Haram ka iya haifarwa a yankin.

Gwamnatin Bornon ta kuma nemi afuwar, jama’ar da matakin ya shafa, dangane da matsi ko takura da dokar zata haifar musu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.