Najeriya
Amurka ta tabbatar da cinikin saidawa Najeriya jiragen yaki 12
Kasar Amurka ta amince ta saidawa Najeriya jiragen yakin sama 12 kirar Super Tucano A-29, domin yaki da kungiyar Boko Haram.
Wallafawa ranar:
Talla
Cikin sanarwar da ta rabawa manema labarai, rundunar sojin Najeriyar ta ce Jakadan Amurka a kasar ya mika takardun cinikin ga shugaban rundunar sojin sama a ranar Laraba da ta.
Sanarwar tace ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta amince da cinikin kuma nan da ranar 20 ga watan Fabarairun shekara mai kamawa ake saran kammala biyan kudin.
Bayan jiragen 12, cinikin ya kunshi wasu makaman rokoki da bama bamai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu