Isa ga babban shafi
Najeriya

MTN ya biya Najeriya Naira biliyan 80

Kamfanin sadarwa na MTN ya biya gwamnatin Najeriya Naira biliyan 80 daga cikin tarar Naira biliyan 330 bayan kamfanin ya ki rufe layukan mutane fiye da miliyan biyar da ba su yi rajistar layinkansu ba. 

Ofishin kamfanin MTN da ke birnin Legas na Najeriya
Ofishin kamfanin MTN da ke birnin Legas na Najeriya 8brand.co
Talla

Ministan sadarwa na kasar Adebayo Shittu ne ya sanar da hakan a taron manema labarai da aka gudanar a birnin Abuja.

An ci tarar MTN Dala biliyan biyar da miliyan biyu kafin daga bisani a rage zuwa Naira biliyan 330 bayan cimma matsaya a tsakanin bangarorin biyu, kuma wannan shi ne karon farko da kamfanin ke fara biyan tarar da aka tsara zai biya a tsawon shekaru uku.

A watan Oktobar 2015 ne hukumar kula da kafofin sadarwa NCC, ta yanke hukunci tare da cin kamfanin tara bisa laifin kin yanke layukan.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.