Isa ga babban shafi
Najeriya

NCC ta dakatar da karin kudin data a Najeriya

Hukumar da ke sa ido a kan kamfanonin sadarwa ta Najeriya, NCC, ta dakatar da shirinta na kara kudin data ga masu amfani da wayar Salula sakamakon sukar da suke sha daga wurin jama'a.

'Yan Najeriya sun soki matakin karin kudin data a wayar Salula a Najeriya
'Yan Najeriya sun soki matakin karin kudin data a wayar Salula a Najeriya
Talla

A zantawarsa da RFI Hausa shugaban hukumar ta NCC, Farfesa Umar Garba Dambata, ya ce sun umarci kamfanonin sadarwa kasar su dakatar da karin kudin datar da ya kamata ya soma aiki daga gobe 1 ga watan Disamba, zuwa nan gaba.

Farfesa Umar ya ce daukan matakin zai basu daman tuntubar masu ruwa da tsaki da sauraron ra’ayoyin masu amfanin da layukan salulan.

Kafin wannan mataki Majalisar dattijen Najeriya ta umarci hana Karin, yayin da ‘yan Najeriya ke cewa wani yunkuri ne takaita fadin albarkacin bakinsu a shafukan sadarwa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.