Gwamnati ta janye tuhumar da ake wa Saraki da Ekweremadu
Gwamnatin Najeriya ta janye tuhumar da ta ke shugaban Majalisar Dattawan Bukola Saraki da Mataimakinsa Ike Ekweremadu na sauya dokoki domin amun damar darewa shugabancin majalisar.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Wani jami’in ma’aikatar shari’ar kasar Odubu Loveme ya gabatar da takardar janye karar a gaban kotun ranar Alhamis.
Gwamnatin ta zargi Bukola Saraki da mataimakinsa Ike Ekweremadu da kuma tsohon kakakin majalisa Salisu Maikasuwa da mataimakinsa Ben Etifuri da sauya dokokin da ya bai wa Saraki damar hawa kujerar shugabancin Majalisar.
Su dai wadanda ake zargin sun ki amincewa da tuhumar a shari’ar da ta dauke hankalin 'Yan Najeriya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu