Isa ga babban shafi
Najeriya

Masana Na Fargaban Za'a Fuskanci Yunwa a Arewa maso Gabashin Najeriya

Ayarin masana dake sa idamu a kan rikicin da ake yi a yankin arewa maso gabashin Najeriya na cewa akwai alamun za'ayi fama da fari a yankin saboda kazamin ta'adi da ‘yan kungiyar Boko Haram suka janyo wa yankin.

Daruruwan mata 'yan gudun hijira a sansanoni a jihar Borno na Najeriya
Daruruwan mata 'yan gudun hijira a sansanoni a jihar Borno na Najeriya AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Ayarin masanan dake zaune a Amurka, karkashin suna 'Famine Early Warning Systems Network'  sun fadi a wata sanarwa cewa mutane sama da miliyan uku na cikin wani hali a yankin kuma su na bukatar taimako.

Kungiyoyi irin wannan kan ayyana za’a sami fari muddin suka lura cewa kashi 20% na yankin da ake zance na fama da matsalar rashin abinci, ga matsanancin matsalolin rashin lafiya da sauran matsalolin rayuwa.

Dubban rayukan jama'a ne dai suka salwanta a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya sakamakon hare-hare na 'yan kungiyar Boko Haram.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.