NLC ta janye yajin aiki a Najeriya
Kungiyar kwadago ta Najeriya karkashin shugabanta Ayuba Waba, ta janye yajin aikin game gari da ta fara a ranar labarar da ta gabata.
Wallafawa ranar:
Kungiyar ta shiga yajin aikin ne domin nuna adawarta da matakin da gwamnatin kasar ta dauka na kara farashin man fetir zuwa naira 145 daga Naira 86 a kan kowacce lita guda.
Wannan al’amari dai ya haifar da cecekuce a dukkanin fadin kasar, inda wasu ke marhaba da matakin janye tallafin man fetir yayin da wasu kuwa ke nuna akasin haka.
Gabanin janye yajin aikin a wannan Lahadin, sai dai kungiyar ta yi ta zanta wa da wakilan gwamnati domin cimma matsaya akan batun.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu