Isa ga babban shafi

Adadin wadanda suka mutu a hare-haren Isra'ila a Gaza ya kusan dubu 25 - Hamas

A yayin da Isra’ila ke ci gaba da kai hare hare yankin Zirin Gaza a kokarin da take na kakkabe  mayakan Hamas, ma’aikatar lafiyar yankin ta ce adadin wadanda suka   mutu ya zuwa yanzu ya tasam ma dubu 25.

Wani bangare na birnin Khan Younis kena da Isra'ila ke ci gaba da kai hare-hare.
Wani bangare na birnin Khan Younis kena da Isra'ila ke ci gaba da kai hare-hare. AFP - -
Talla

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Fira ministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, wanda  ke  shan caccaka daga cikin kasarsa ya yi watsi da kiran samar da kasar Falasdinu bayan wannan yaki.

 

Ma’aikatar lafiyar Gaza ta ce akalla mutane 165 ne suka mutu sakamakon hare-haren Israila a cikin sa’o’i 24, adadin da ya ninka wanda aka samu a ranar Juma’a.

Kamfanin dillancin labaran Faransa ya ruwaito cewa an yi  ta jin kararrakin harbe-harbe da fashe-fashe  a kudancin Zirin Gaza, musamman a birnin Khan Younis.

 

Tun bayan harin da mayakan Hamas suka kai Isra’ila a ranar 7 ga watan Oktoban  shekarar 2023 ne fada ya barke tskanin kasar ta Yahudu da mayakan Hamas, wadda ta sha alwashin kakkabe mayakan, lamarin da ya  sa ta ke ta kai hare-hare ba kakkautawa a yankin Zirin Gaza.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.