Isa ga babban shafi

Hamas za ta ci gaba da sakin wadanda ta ke garkuwa da su

Hamas za ta ci gaba da aiki da yarjejeniyar sakin wadanda take garkuwa da su a daren Asabar din nan bayan da aka warware  matsalar da ta taso a game da shigo da kayan agaji arewacin Gaza, sakamakon shiga tsakani da Masar da Qatar suka yi.

Wasu daga cikin wadanda Hamas ta saki bayan yarjejeniyarta da Isra'ila.
Wasu daga cikin wadanda Hamas ta saki bayan yarjejeniyarta da Isra'ila. via REUTERS - AL-QASSAM BRIGADES, MILITARY WIN
Talla

Wani jami’in Falasdinu da ke da masaniya a game da yunkurin diflomasiyar ya ce Hamas za ta ci gaba da  mutunta kwarya-kwaryar yarjejeniyar ta kwanaki hudu kamar yadda ta kulla da Isra’ila, tsagaaita wuta ta farko da aka cima tun da aka fara wannan rikici a ranar 7 ga watan Oktoba.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajenn Qatar, Majed Al Ansari ne ya tabbatar da warware wannan matsalar da ta taso daga baya a dandalin sada zumunta, inda ya ce a cikin wannan dare  Hamas za ta saki Yahudawa 13 da wasu ‘yan kasashen waje 7, a yayin da Isra’ila za ta sakar mata Falasdinawa 39.

Tun da farko, Jagorancin mayakan Hamas ta ce za a jinkirta sakin wadanda take garkuwa da su idan Isra’ila ba ta  yi biyayya da ilahirin yarjeniyoyin da aka cimma a game da sakin Falasdinawan da take tsare da su a gidajen yarinta.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.