Isa ga babban shafi

Hamas ta jinkirta sakin wadanda take garkuwa da su

Kungiyar Hamas ta yanke shawarar jinkirta sakin rukuni na biyu na wadanda ta ke garkuwa da su a Asabar din nan kamar yadda aka tsara, har sai Isra’ila ta cika alkawarinta na barin manyan motoci dauke da kayayyakin agaji su shiga Gaza.

Daya  daga cikin wadanda Hamas suke garkuwa da su da aka saki a ranar 24 ga watan Nuwamba.
Daya daga cikin wadanda Hamas suke garkuwa da su da aka saki a ranar 24 ga watan Nuwamba. Al Qahera News/via REUTERS - REUTERS TV
Talla

Jagorancin mayakan Hamas ta ce za a jinkirta sakin wadanda ake garuwa da su idan Isra’ila ba ta  yi biyayya da ilahirin yarjeniyoyin da aka cimma a game da sakin Falasdinawan da take tsare da su a gidajen yarinta.

Babu wani martini daga Isra’ila a game da wannan mataki na Hamas.

Tun da farko wani kakakin sojin Isra’ila ya ce idan har babu wani abin da ya sauya, ana sa ran sakin mutane 13 daga cikin wadanda Hamas ta yi garkuwa da su a Asabar din nan. Ya ce Isra’ila za ta saki fursunoni Falasdinawa 39.

A karkashin wannan yarjejeniya da aka kulla tsakanin Hamas da Isra’ila, za a yi musayar jimillar mutane 50 wadanda aka yi garkuwa da su da Falasdinawa 150 da ke gidajen yarin Isra’ila a cikin kwanaki 4.

Wannan koma-baya da aka samu a Asabar dinnan na zuwa ne ‘yan sa’o’i bayan da Masar, wadda ke da iko da mashigin Rafah na Kudancin Gaza ta ce ta ga alamar  cewa akwai yiwuwar tsawaita kwarya-kwaryar tsagaita wutar da aka cimma tsakanin bangarorin biyu.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.