Isa ga babban shafi

Sojojin Isra'ila sun bada sa'a guda ga kowa ya fice daga asibitin al-Shifa

Dakarun Isra’ila sun umurci llikitoci da marasa lafiya  daa ma wadanda yakin da ake yi ya daidaita so fita daga asibitin al-Shifa, inda  suka ba su sa’a da su yi haka su na mai tilasta su da bakin bindiga su bi umurnin nasu, kamar yadda majiyoyi daga asibitin suka bayyana.

Photo diffusée par l'armée israélienne le 15 novembre 2023 qui montre un soldat se tenant à l'extérieur de l'hôpital al-Chifa.
Wasu dakarun Isra'ila a wajen asibitin al-Shifa, ranar 15 ga watan Nuwamba, 2023. AFP - -
Talla

Amma aa wani sako da ta  wallafa a shafintaa na dandalin sada zumunta na X, wanda aka sani da Twitter kafin yanzu, rundunar sojin Isra’ilar ta musanta tilasta wa wani barin wannan asibitin, tana mai cewa sojojinta sun karbi bukatar da shugaban asibitin ya mika musu ne ta cewa su bari wadanda ke bukatar ficewa daga asibitin su fita.

Sai dai shugaban hukumar da ke kula da asibitoci a Zirin Gaza, Mohammed Zaqout,  ya jaddada cewa sojin Isra’ila ne suka tilasta musu barin asibitin da bakin bindiga.

Mutane sama da dubu 7 ne ke cikin wannan asibiti, cikinsu har da marasa lafiya da suka hada da jarirai, wadanda ke halin rai-kwakwai-mutu-kwakwai, tun bayan da dakarun Isra’ila suka yi wa asibitin.

Tun da farko  wani likita  a asibitin al-Shifa ya ce ba zai yiwu a fice daga asibitin ba, amma daga baya rahotanni sun ce an fara ffitar da mutane daga asibitin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.