Isa ga babban shafi

Iran ta ce tana fatan musayar fursunoni da Amurka nan ba da jimawa ba

Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta ce tana fatan tabbatuwar musayar fursunoni da Amurka a Litinin, matsawar ta samu kudaden da suka kai dala biliyan 6, wanda kawar Amurka, Koriya ta Kudu  ta rike mata.

Shugaban Iran, Ebrahim Raisi.
Shugaban Iran, Ebrahim Raisi. AFP - BAY ISMOYO
Talla

A karkashin yarjejeniyar, wadda Amurka  da Iran suka tabbatar da wanzuwar ta a baya, Iran za ta saki Amurkawa 5 da ke hannunta, kana Amurka ta saki Iraniyawa 5 da ta ke tsare da su.

Kasashen  biyu, wadanda ba sa jituwa da juna sun kuma amince da batun sakin kudaden da suka kai dala biliyan 6 mallakin Iran, wanda Koriya ta Kudu ta rike saboda takunkuman Amurka, wanda za tura shi zuwa asusun ajiyar Iran don sayen kayayyakin agaji.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Nasser Kanani ya shaida wa wani taron manema labarai a Iran cewa za a yi musayar  fursunonin a rana guda, inda za a saki Iraniyawa 5, wadanda Amurka ke tsare daa su.

Kasar Qatar ce ta shirya wannan musayar fursunoni, saboda Iran ba ta da dangantakar diflomasiyya da Amurka.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.