Isa ga babban shafi

Mutane 9 sun mutu a hare-haren da dakarun Isra’ila suka kai yankin Falasdinu

Mutane 9 sun hallaka sakamakon hare-haren da dakarun Isra’ila suka kaddamar a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke yankin Jenin na yamma da kogin Jordan. 

Mutane 8 sun hallaka sakamakon hare-haren da dakarun Isra’ila suka kaddamar a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke yankin Jenin.
Mutane 8 sun hallaka sakamakon hare-haren da dakarun Isra’ila suka kaddamar a wani sansanin ‘yan gudun hijira da ke yankin Jenin. © AP / Ohad Zwigenberg
Talla

 

Kafin wannan hari, sai da dakarun na Isra’ila suka kashe wani matashi dan shekaru 21 mai suna Mohammed Hasanein a mashigin Ramallah da ke tsakiyar Faladinu, kamar yadda ma’aikatar lafiyar kasar ta tabbatar. 

Mazauna yankin sun tabbatarwa manema labarai cewa Isra’ilan ta kai hare-hare kusan 10 kan yankin na Jenin cikin daren jiya Lahadi, lamarin da ya sanya hayaki turnuke sararin samaniya tare da rushe gine-gine. 

Tun farko dai sojojin Isra’ilan sun zagaye sansanin 'yan gudun hijirar da tankokin yaki fiye da 10, kafin daga bisani suka fara luguden wuta lamarin da ya lalata gine-ginen da ke wajen. 

Bayan ta fitar da jerin mutanen da suka mutu sanadin hare-haren, ma’aikatar lafiyar Palasdinu ta kuma ce fiye da Falasdinawa 30 ne suka gamu da munanan raunuka. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.