Isa ga babban shafi
Yakin Yemen

Yarjejeniyar tsagaita wuta ta fara aiki a Yemen

Ranar Asabar rundunar  kawance sojin da Saudiya ke jagoranta a yakin yemen da kuma ‘yan tawayen Houthi suka ajiye makamansu, bayan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta gama gari, irinta  ta farko tun shekarar 2016.

Wasu yara a birnin Aden na kasar Yemen.
Wasu yara a birnin Aden na kasar Yemen. AFP - SALEH AL-OBEIDI
Talla

Yarjejeniyar tsagaita wutar da bangarorin biyu suka cimma za ta shafe watanni biyu tana aiki, daga yau, ranar 1 ga watan Ramadan.

Yakin da aka shafe shekaru ana gwabzawa a Yamen ya yi sanadin mutuwar dubban mutane gami da raba wasu miliyoyi da muhallansu, lamarin da ya janyo matsalar ayyukan jin kai mafi muni a duniya, rahoton da Majalisar Dinkin Duniya.

A baya dai yarjeniyoyin tsagaita wutar da aka kulla a yakin na Yemen ba su yi wani tasiri ba.

Wata kididdigar Majalisar Dinkin Duniya ta nuna cewar, a cikin mutane kusan miliyan 32, miliyan 23 da kusan rabi na bukatar agajin jin kai, miliyan 12 da dubu 900 kuma na cikin tsananin bukata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.