Isa ga babban shafi
Yemen

An kashe mutane 70 a wani hari ta sama da aka kai kan gidan Yari a Yemen

Akalla mutane 70 suka mutu a wani hari ta sama da rundunar sojojin kawancen Larabawa da Saudiya ke jagoranta ta kai kan wani gidan Yari a Yemen, yayin da kuma akalla yara uku suka mutu a wani harin bam na daban a kasar ta Yemen.

Yadda hari ta sama ya ragargaza gidan Yarin birnin Sa'da dake arewacin kasar Yemen.
Yadda hari ta sama ya ragargaza gidan Yarin birnin Sa'da dake arewacin kasar Yemen. AFP - -
Talla

'Yan tawayen Huthi sun fitar da wani faifan bidiyo da ke nuna gawarwaki a cikin baraguzan ginin da farmakin jiragen yakin ya rusa, a yankin tsakiyar birnin Sa’da da ke arewacin Yemen.

Kungiyar ayyukan jin kai ta ‘Save the Children’ ta ce a wani na dabam kuma da aka kai a kudancin birnin Hodeida mai tashar jiragen ruwa, yara 3 sun mutu a lokacin da jiragen yakin kawancen sojojin Larabawa suka kai hari kan wata cibiyar sadarwa, a daidai lokacin da kananan yaran ke wasa a kusa da wurin.

Cikin wata sanarwa da ya fitar, ofishin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya ya ce rahotannin yawaitar kai hare-hare ta sama kan yankunan da ke da yawan jama'a fararen hula abu ne mai matukar tayar da hankali.

Su kuwa wasu kungiyoyin ayyukan agaji takwas da ke aiki a Yemen, sun bayyana firgita ne da labarin kashe mutane sama da 70 da suka hada da bakin haure da mata da kananan yara a gidan Yarin birnin Sa’ada, abinda suka bayyana a matsayin rashin mutunta rayukan fararen hula.

Daga bisani dai rundunar kawancen sojojin kasashen Larabawan ta musanta kai farmakin da yayi sanadin mutuwar mutane 70 a birnin Sa'da

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.