Isa ga babban shafi
Yemen

'Yan Houthi sun zartas da hukuncin kisa kan mutane 9 da suka kashe jagoran su

'Yan tawayen Huthi da ke Yemen zartas da hukuncin kisa kan wasu mutane 9 a yau Asabar, wadanda suka samu da hannu a kisan daya daga cikin manyan shugabanninsu, yayin wani hari ta sama da Saudiyya ta jagoranta a shekarar 2018.

Wasu daga mutanen da 'yan tawayen Houthi suka zartaswa da hukuncin kisa bayan da aka same su da laifin hannu a kisan jagoran su na siyasa Saleh al-Sammad shekaru uku da suka gabata. 18 ga Satumba, 2021.
Wasu daga mutanen da 'yan tawayen Houthi suka zartaswa da hukuncin kisa bayan da aka same su da laifin hannu a kisan jagoran su na siyasa Saleh al-Sammad shekaru uku da suka gabata. 18 ga Satumba, 2021. © AFP
Talla

Kafin mutuwar sa Saleh al-Sammad shi ne shugaban majalisar kolin Siyasar Houthi, wanda rashin sa ya zamewa 'yan tawayen da ke samun goyon bayan Iran koma baya.

Mutanen 9 da ‘yan tawayen na Houthi suka harbe, na cikin 16 da kotun su ta samu da hannu a kisan jagoran na su.aaa

Daga cikin sauran mutane 7 da aka yankewa hukuncin kisan duk da basa nan kuma  akwai Yarima mai jiran gadon sarautar Saudiyya Mohammed bin Salman da tsohon shugaban Amurka Donald Trump.

An kashe Sammad a watan Afrilun shekarar 2018 tare da wasu mutane shida a wani hari ta sama a lardin Hodeida da ke Yemen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.