Isa ga babban shafi

Faransa ta gargadi 'yan kasarta yin balaguro zuwa yankin Gabas ta tsakiya

Faransa ta gargadi ‘yan kasar ta game da tafiya zuwa kasashen Iran, Lebanon, Isra’ila da kuma yankunan Palasdinu a halin yanzu.

Shugaban Faransa Emmanuel Nacron kenan.
Shugaban Faransa Emmanuel Nacron kenan. © LUDOVIC MARIN / AFP
Talla

Ministan harkokin wajen kasar Stephane Sejourne ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa a halin da ake ciki yana da matukar hadari yan kasar su ziyarci wadannan kasashe.

Wannan gargadi na zuwa ne bayan da Iran ta yi barazanar kai munanan hare-hare zuwa Isra’ila matsayin ramuwar gayyar da ta kai kan ofishin jakadancin ta dake Syria da yayi sanadin mutuwar mutune 7 ciki har jana-janar din soja guda biyu.

Wannan na nuna yadda rikici ke kara rincahbewa a gabas ta tsakiya, dalilin da ya sanya Faransar daukar aniyar fara kwashe jakadunta da ke Iran tare da Iyalan su, kuma ba za’a sake tura wani bafaranshe aiki a wadannan kasashe da aka lissafa ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.