Isa ga babban shafi

Bukatun Isra'ila na tsagaita wuta ba su yi dai-dai da na Falasdinawa ba - Hamas

Kungiyar Hamas ta ce bukatun da Isra'ila ta gabatar na tsagaita wuta a yakin da suke yi a Gaza, ba su yi dai-dai da bukatun bangaren Falasdinawa ba, amma za ta kara yin nazari kan tayin tare da mika matsayarta ga masu shiga tsakani.

Kungiyar Hamas ta ce bukatun da Isra'ila ta gabatar na tsagaita wuta a yakin da suke yi a Gaza, ba su yi dai-dai da bukatun bangaren Falasdinawa ba.
Kungiyar Hamas ta ce bukatun da Isra'ila ta gabatar na tsagaita wuta a yakin da suke yi a Gaza, ba su yi dai-dai da bukatun bangaren Falasdinawa ba. AP - Leo Correa
Talla

A karshen wata tattaunawa da wakilan bangarorin sukayi a birnin Cairo ne dai kasashen Masar da Qatar, da ke shiga tsakani suka mika wa Hamas bukatar Isra’ila kan cimma yarjejeniyar tsagaita wuta, bayan kwashe watanni 7 ana kai hare-hare yankin na Gaza.

Sai dai wasu al’ummar yankin Gaza sun ce Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare ta sama a tsakiya da kuma Kudancin Gaza a jiya Talata, ciki kuwa har da harin da ya hallaka iyalai 14 a Al-Nusseirirat.

Palestinians inspect the site of an Israeli airstrike on a building, amid the ongoing conflict between Israel and the Palestinian Islamist group Hamas, in Rafah, in the southern Gaza Strip April 2, 20
Wasu daga cikin wuraren da hare-haren Isra'ila suka shafa a Gaza. REUTERS - Mohammed Salem

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya tabbatar da shirinsu na kai hari ta kasa a yankin Rafah, inda sama da fararen hula miliyan daya ke samun mafaka, duk kuwa da matsin lambar da kasashe suka yi masa na kaucewa hakan.

A wannan tattaunawa ta karshe da bangarorin suka yi a birnin Cairo na kasar Masar, ta samu halartar shugaban Hukumar Leken Asirin Amurka William Burns, sai dai kuma an gaza cimma matsaya.

A karkashin  yarjejeniya da za a cimma, Hamas na bukatar ganin Isra’ila ta daina kai hare-hare yankin Gaza tare da barin mutane su koma gidajensu da suka yi saura.

To sai dai a nata bangaren, Isra’ila na kokarin ganin ta kubutar da mutanenta da Hamas tayi garkuwa da su a ranar 7 ga watan Oktoban bara, tare kuma da kawo karshen mulkin da Hamas ke yi a yankin tun a shekarar 2007.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.