Isa ga babban shafi

'Yan ci rani kusan 100 sun yi batan dabo a tekun Meditareniya cikin 2024

Hukumar kula da ‘yancirani ta Majalisar Dinkin Duniya ta bayyana cewa Kusan bakin haure 100 ne suka mutu ko kuma suka bace a tsakiya da gabashin tekun meditereniya tun farkon shekarar 2024, wanda ya ninka adadin da aka samu a bara a irin wannan lokacin. 

A cewar hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta duniya, fiye da ‘yan-cirani dubu 3 ne suka mutu ko kuma suka bace cikin shekarar nan a kokarinsu na tsallaka Nahiyar Turai daga Libya.
A cewar hukumar kula da ‘yan gudun hijira ta duniya, fiye da ‘yan-cirani dubu 3 ne suka mutu ko kuma suka bace cikin shekarar nan a kokarinsu na tsallaka Nahiyar Turai daga Libya. REUTERS/Ahmed Jadallah
Talla

Hukumar ta IOM tayi wannan bayani ne a wani babban taro dake gudana a birnin Rom na kasar Italiya, wanda ya samu halartar gomman shugannin Afirka da na Turai domin tattauna batutuwan ci gaban tattalin arziki da kuma hanyoyin magance matsalar bakin haure dake tafiya Turai.

Bayanan binciken ayyukan da aka gudanar game da mutuwa ko bacewar bakin haure a baya bayannan an samu mutane dubu 3 da 41 da ko sun bace ne ko kuma sun mutu tekun meditereniya, a shekarar da ta gabata a kokarinsu na shiga turai.

A farko farkon wannan wata ne  wasu ‘yancirani 40 ‘yan kasar Tunisia suka yi batan dabo a wani babban kwale kwale daya nufi gabar tekun Italiya.

Tunisia dai ta maye gurbin Libya a matsayin wata muhimmiyar kafa da bakin haure ke bi domin ficewa kasashen saboda tserewa taluaci ko kuma yake-yake.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.