Kisan da aka yi wa yara a Gaza shi ne irinsa na farko a tarihi
Adadin kananan yaran da aka kashe a Yammacin Kogin Jordan da kuma Gabashin Birnin Kudus a bana, ya kai wani mataki da ba a taba ganin irinsa ba kamar yadda Hukumar Kula da Kananan Yara ta Majalisar Dinkin Duniya, UNICEF ta bayyana.
Wallafawa ranar:
Darektar UNICEF a yankin Gabas ta Tsakiya da Arewacin Afrika, Adele Khodr ta bayyana cewa, an kashe kananan yara 83 a cikin makwanni 12 da suka gabata, adadin da ya rubanya wanda aka samu a shekarar 2022.
Sama da kananan yara 576 ne aka raunata, sannan aka tsare wasu da dama kamar yadda darektar ta bayyana a cikin wata sanarwa.
Babbar Jami’ar ta UNICF ta koka kan yadda kasashen duniya suka zura ido suna kallon mummunan abin da ke faruwa a Zirin Gaza, inda yaran da ke Yammacin Kogin Jordan ke gamuwa da bala’i, ganin yadda suke cikin tsoro da bakin ciki a kodayaushe.
Rahotanni na cewa, fargaba ta dabaibaye rayuwar yau da kullum ta yaran, inda har wasu daga cikinsu ke tsoron zuwa makaranta ko kuma gudanar da wasa a waje saboda barazanar harbe-harben bindiga.
Yanzu haka hukumar ta UNICEF ta bayyana damuwarta game da hakkokin kananan yaran da ake takewa a Yammacin Kogin Jordan da kuma Gabashin Birnin Kudus, tana mai kira da a samar musu da tsaro da kariya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu