Isa ga babban shafi

Kotu ta tuhumi Trump da yunkurin sauya sakamakon zabe

Bayan shafe shekaru biyu suna gabatar da bincike, masu gabatar da kara a Amurka sun tuhumi tsohon shugaban kasar Donald Trump da laifin yunkurin sauya sakamakon zaben shugaban kasar na jihar Georgia da ya gudana a shekarar 2020, bayan da sakamakon zaben ya nuna cewa Trump din ya sha kashi a hannun dan takarar jam’iyyar Democrats, Joe Biden. 

An tuhumi tsohon shugaban Amurka Donald Trumpda kokarin karkata sakamakon zaben 2020
An tuhumi tsohon shugaban Amurka Donald Trumpda kokarin karkata sakamakon zaben 2020 REUTERS - Carlos Barria
Talla

Masu gabatar da kara a Atlanta sun zargi  Trump da aikata manyann laifuka 13, abin da ya kara jefa ci cikin matsaloli a gaban kuliya, kuma ya saka burinsa na neman shugabancin kasar a karo na biyu cikin hatsari. 

Wasu karin mutane 118 suna fuskantar wadannan tuhume-tuhume  a kan wannan bincike da ake gudanarwa, ciki har da lauyansa, Rudy Giulianni, wanda  yake da hannu wajen matsa lamba a kan sakamakon zaben shekarar 2020, da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasar Amurka, Mark Meadows. 

Trump tare da sauran wadanda ake zargi  sun ki amincewa da cewa, Trump ya fadi zabe, kuma da gangan suka rika cikin kulla  munakisar sauya sakamakon zaben ta inda zai nuna cewa, shi Trump din ne ya ci zabe, kamar yadda takardar zargin ta bayyana. 

Lauyoyin da aka ambaci sunayensu a kan wannan dambarwa sun ki cewa uffan, wasu daga cikinsu kuma ba a same su ba don  yi wa manema labarai bayani. 

Wannan  batu da ya ke nema ya kai Trump ya baro dai ya samo asali ne daga zantawa ta wayar tarho da tsohon shugaban ya yi da shugaban Hukumar Zaben Jihar Georgia, Brad Raffensperger, inda  yake bukatar sa ya yi aringizon kuri’u da za su goge rashin nasarar da ya yi a jihar. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.