Isa ga babban shafi

Girgizar kasa a gabashin China ta ruguza gidaje tare da jikkata akalla 21

Wata girgizar kasa a gabashin China ta rusa gidaje tare da raunata akalla mutane 21, kamar yadda kafafen yada labaran kasar suka bayyana, amma ba a samu asarar rai ba.

Yadda duwatsu ke fadowa a hanyar Lengki da ke wajen kauyen Luding na kasar China.
Yadda duwatsu ke fadowa a hanyar Lengki da ke wajen kauyen Luding na kasar China. AP
Talla

Girgizar kasar mai karfin maki 5.5 ta afku a kusa da birnin Dezhou mai tazarar kilomita 300 kudu da birnin Beijing, babban birnin kasar, da misalign karfe 2:30 na safe.

Hukumomin kasar sun ce, an ji alamar motsin kasa a wasu sassan birnin Beijing, amma ba a samu barna a babban birnin kasar ba.

Yankin Dezhou da kewayen birnin na da kusan mutane miliyan 5.6, a cewar hukumar kula da yawan jama'a ta kasar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.