Isa ga babban shafi

China da Amurka zasu soma tattaunawa kan dumamar yanayi a gobe litinin

Jakadan Amurka kan sauyin yanayi John Kerry ya isa birnin Beijing a yau lahadi , da nufin fara tattaunawa da kasar China kan dumamar yanayi, yayin da manyan kasashen biyu suka sake yin shawarwari mai zurfi bayan shafe watanni ana takun saka.

Wasu daga cikin manyan kamfanoni da ke gurbata muhali a Duniya
Wasu daga cikin manyan kamfanoni da ke gurbata muhali a Duniya © Fabrice Coffrini / AFP
Talla

John Kerry, wanda ke yin ziyararsa ta uku zuwa kasar China, na zuwa ne a daidai lokacin da ake ganin tasirin sauyin yanayi musamman a doron kasa, inda ake fama da zafi a sassa da dama na duniya.

John Kerry, a wani zaman kasashen duniya kan yanayi
John Kerry, a wani zaman kasashen duniya kan yanayi REUTERS - MOHAMMED SALEM

Daga cikin yankunan dake fama da zafi ba a bar kasar China ba kuma babban birninta na Beijing yana fuskantar yanayin zafi kusan ma'aunin Celsius 40 tsawon makonni.

John Kerry wanda zai kasance a kasar China har zuwa ranar Laraba, zai gana da takwaransa Xie Zhenhua.

China da Amurka manyan masu gurbata muhalli na duniya, manyan kasashen duniya biyu na farko  da suka kauracewa tattaunawa  kan yanayin  kusan shekara guda, domin a  watan Agustan da ya gabata, China ta dakatar da tattaunawa kan wannan batu don nuna adawa da ziyarar da shugabar majalisar wakilan Amurka ta yi a Taiwan Nancy Pelosi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.