Isa ga babban shafi

Rasha ta girke makamin nukiliya a Belarus don afka wa Ukraine

Shugaban Belarus Alexander Lukashenko ya bayyana cewa, Rasha ta fara girke makaman nukiliya a cikin kasar wadda ke zama makwabciyarta kuma aminyarta, matakin da ke zuwa bayan shugaba Vladimir Putin ya sanar da wannan shirin a cikin watan Maris.

Tuni kasashen yammacin duniya suka caccaki Rasha kan shirinta na girke makamin nukiliya a Belarus don far wa Ukraine.
Tuni kasashen yammacin duniya suka caccaki Rasha kan shirinta na girke makamin nukiliya a Belarus don far wa Ukraine. © AP
Talla

Kawo yanzu babu sanarwar da Rasha ta fitar da kanta da ke nuna cewa, lallai ta fara jibge makamanta na nukiliya a makwabciyar kasarta ta Belarus.

Sai dai shugaba Lukashenko ya shaida wa taron manema labarai a yayin wata ziyara da ya kai birnin Moscow cewa, an fara aikewa da makaman na nukiliya.

Shugaban na Belarus ya ce, takwaransa na Rasha, Putin ya shaida massa cewa, tun a ranar Laraba, ya sanya hannu kan dokar izinin girke makamin na nukiliya.

Lukashenko dai ya bai wa Rasha kan iyakar kasarsa domin ta zama wani sansanin kaddamar da farmaki cikin Ukraine.

Belarus na da iyaka da Ukraine da kuma kasashen Poland da Lithuania da suka kasance mambobi a Kungiyar Tarayyar Turai da kuma Kungiyar Tsaro ta NATO.

A cikin watan Maris ne shugaba Putin na Rasha ya sanar cewa, zai girke makamin nukiliya mai cin garejen zango a kan iyakar Belarus, lamarin da ya janyo masa caccaka daga kasashen yammacin duniya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.