Isa ga babban shafi

Ukraine za ta kwato yankunanta da Rasha ta kwace - NATO

Sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg ya bayyana aniyarsa ta ganin Ukraine ta sake kwatoyankunan ta da Rasha ta mamaye ganin yadda kawayen kasar suka sha alwashin ci gaba da bata tarin taimako a wajen wani taron da Amurka ta jagoranta. 

Sakatare Janar na kungiyar tsaro ta NATO kenan Jens Stoltenberg, daga hagu, tare da sshugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy, yayin wata ganawa a birnin Kyiv, Ukraine, ranar 20 ga watan Afrilu, 2023.
Sakatare Janar na kungiyar tsaro ta NATO kenan Jens Stoltenberg, daga hagu, tare da sshugaban Ukraine Volodymyr Zelenskyy, yayin wata ganawa a birnin Kyiv, Ukraine, ranar 20 ga watan Afrilu, 2023. AP
Talla

Taron wanda ya samu halartar wakilan kasashe 50 da akayi a kasar Jamus, ya tattauna batutuwa da dama da suka hada da karin makamai da kayan yaki da kuma sabbin dabarun zamani da za’ayi amfani da su wajen samun nasarar yakin. 

Stoltenberg ya shaidawa manema labarai cewar yanzu haka yana da yakinin cewar dakarun Ukraine na cikin yanayin da zasu iya kwato yankunan su da aka kwace. 

Sakataren tsaron Amurka Lloyd Austin wanda ke jagorancin taron yace batutuwa 3 suka dauke hankalin mahalarta taron da suka hada da samar da tsaron sama a Ukraine da makamai da kuma dabarun zamani. 

Sai dai kakakin Rasha Dmitry Peskov yayi watsi da taron, inda ya zargi NATO da yaudarar Ukraine. 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.