Isa ga babban shafi

Guterres ya caccaki manyan kasashe kan ci da gumin kanana

Magatakardan Majalisar Donkin Duniya Antonio Guterres ya caccaki kasashe masu hannu da shuni da arzikin makamashi a game da yadda suke ci da gumin takwarorinsu matalauta ta wajen tsawwala musu kudin ruwa tare da ruguza farashin mai.

Magatakardan Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres.
Magatakardan Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres. REUTERS - TIKSA NEGERI
Talla

Da yake jawabi a Doha, babban birnin Qatar,  Speaking Guterres ya shaida wa jagororin kasashe marasa galihu sama da 40 cewa,  kamata ya yi kasashe masu  karfin arziki  su sama musu dala biliyan dubu 5 duk shekara don taimaka wa wadanda suka tauye a bangaren bunkasar tattalin arziki da samara da mahimman ayyuka.

An saba gudanar da taron  koli na kasashen da suka   fi koma baya a fannin ci gaba bayan duk shekaru 10, amma aka daga har sau,  tun a shekarar 2021 saboda annobar  Coronavirus.

Afghanistan da Myanmar, 2 daga ckin kasashe  marasa  karfin tattalin arziki da ba su halarci wannan taro na Doha  ba, saboda rashin amincewa da gwamnatocinsu a majalisar dinkin duniya.

Babu wani shugaba na daya daga cikin manyan kasashe  masu karfin tattalin arziki da ya halarci wannan taro.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.