Isa ga babban shafi

MDD ta karrama mutane dubu 2 da 300 da suka mutu a girgizar kasa

Majalisar Dinkin Duniya ta yi shiru na tsawon minti guda domin karrama sama da mutane  dubu 2 da 300 da suka rasa rayukansu sakamakon ibtila’in girgizar kasa  da ya auku a kasashen Syria da Turkiya a wannan Litinin.

An bayyana girgizar kasar a matsayin mafi muni  cikin shekaru 100 a yankin.
An bayyana girgizar kasar a matsayin mafi muni cikin shekaru 100 a yankin. © AP - Mahmut Bozarslan
Talla

Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya Antonio Guterres ya ce, yanzu haka, tawagarsu na can na bada agaji, yana mai kira ga kasashen duniya da su tallafa wa dubban iyalan mutanen da gagarumin ibtila’in ya rutsa da su.

Kawo yanzu an tattara alkaluman sama da mutane dubu 2 da 300 da suka mutu a kasashen Syria da Turkiya sakamakon girgizar kasar wadda ta auku da asubahin yau, yayin da aka bayyana ta a matsayin mafi muni da aka gani cikin shekaru 100 a wannan yanki.

A kasar Turkiya kadai, hukumomi sun tabbatar da asarar rayukan mutane dubu 1 da 498 , inda kuma a Syria mamatan suka kai 810.

Akwai dai yiwuwar adadin mamatan ya karu, ganin cewa, ana ci gaba da aikin zakulo mutanen da suka makale karkashin buraguzan gine-ginen da suka rushe sakamakon girgizar kasar mai karfin maki 7.8.

Da dama daga cikin mutanen gari sun shiga aikin ceto wadande ke da sauran numfashi, kuma aikin ceton ya fi wahala a Syria saboda karancin kayayyakin aiki a cewar rahotanni.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.