Isa ga babban shafi

Mutane akalla uku ne suka mutu sakamakon ruwan sama a New Zealand

Ruwan sama kamar da bakin kwarya da ba a taba ganin irinsa ba sun yi sanadin mutuwar mutane akalla uku, yayin da ake ci gaba da neman wasu  yanzu haka a Auckland, birni mafi yawan jama'a a New Zealand, sanarwa daga ji Firayim Minista Chris Hipkins a yau asabar.

Zabtarewar kasa a New Zealand
Zabtarewar kasa a New Zealand REUTERS/Anthony Phelps
Talla

'Yan sanda sun ce an gano gawarwaki biyu a yankunan arewacin kasar sannan na uku da ya mutu ya mutu sakamakon zaftarewar kasa kusa da tsakiyar Auckland. 

Filin jirgin saman yankin, mafi girma a kasar, an sake bude wani bangare bayan rufe shi  na wani lokaci a yau asabar. 

 Saboda dalilai na tsaro, an soke wasannin kade-kade da fitaccen mawakin Birtaniya Elton John, wanda aka shirya a filin wasa na Auckland a ranakun Juma'a da Asabar. 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.