Isa ga babban shafi

Turkiya ta yi watsi da sakon jaje da Amurka ta aika mata

Turkiya ta yi watsi da jajen da Amurka ta yi mata game da wani harin bam da ya kashe mutane 6 a birnin Santanbul tare d jikkata wasu gommai, yayin da ake zargin mayakan Kurdawa da kaddamar da farmakin.

Shugaban Turkiya Recep Tayyip Erdogan
Shugaban Turkiya Recep Tayyip Erdogan AP - Vyacheslav Prokofyev
Talla

Shugaba Recep Tayyip Erdogan ya sha zargin Amurka da bai wa mayakan na Kurdawa makamai a yankin arewacin Syria.

Gwamnatin Turkiya ta haramta kungiyar ‘yan tawayen Kurdawa, kuma tana kallon su a matsayin ‘yan ta’adda.

A wani jawabinsa da aka watsa ta kafar talabijin, Ministan Harkokin Cikin Gidan Turkiya Suleyman Soylu ya ce, ba su karbi sakon jaje da ya fito daga ofishin jakadancin Amurka ba.

Tuni hukumomin Turkiya suka ce, sun cafke wata mata ‘yar asalin kasar Syria wadda kuma ke yi wa mayakan Kurdawa aiki bisa zargin ta da hannu wajen kai farmakin na ranar Lahadi.

Koda yake har yanzu, kungiyar Kurdawa ba ta fito karara ta dauki alhakin farmakin ba.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.