Isa ga babban shafi

Masu zanga-zanga 92 aka kashe a kasar Iran - Bincike

Akalla mutane 92 ne aka kashe a kasar Iran sakamakon murkushe masu zanga-zanga, makonni biyu da barkewarta bayan mutuwar Mahsa Amini a hannun ‘yan sandan da suka kama ta.

Mutuwar Mahsa Amini a hannun 'yan sanda na daga cikin abin da ya haifar da zanga-zangar
Mutuwar Mahsa Amini a hannun 'yan sanda na daga cikin abin da ya haifar da zanga-zangar AP
Talla

Wata sanarwa da kungiyar kare hakkin bil'adama mai hedkwata a kasar Norway ta fitar, ta ce shakka babu an ci zarafin masu zanga-zanga a kasar ta Iran

Daraktan kungiyar a Iran, Mahmood Amiry-Moghaddam, ya ce hukumomin kasa da kasa na da alhakin gudanar da bincike kan wannan laifi da kuma hana ci gaba da aikata laifuka daga a kasar.

Alkaluman da aka fitar na baya-bayan nan, sun ce an tabbatar da kashe mutane 83 a zanga-zangar kasar Iran.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.