Isa ga babban shafi

Shugabannin duniya na jimamin rasuwar Sarauniyar Ingila

Shugabannin kasashen duniya sun fara aikewa da sakon ta’aziya ga gwamnatin Birtaniya sakamakon rasuwar Sarauniya Elizabeth ta biyu  wadda ta yi  shekaru 96 a duniya.

Marigayiya Sarauniyar Ingila Elizabeth ta biyu
Marigayiya Sarauniyar Ingila Elizabeth ta biyu AP - Markus Schreiber
Talla

Daga cikin wadanda suka aike da sakon ta’aziyar har da Sakatre Janar na Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, wanda ya bayyana Sarauniya Elizabeth a matsayin wadda ake karramawa a duniya.

Guterres ya ce duniya na girmama marigayiyar saboda karamci da girmamawa da kuma mayar da hankalin da take yi wa jama’a.

Fadar shugaban Amurka ta bayyana matukar kaduwarta da rasuwar Sarauniyar wadda ta bayyana a matsayin shugabar da suke da alaka ta kut-da-kut.

Mai magana da yawun fadar Karine Jean-Pierre ta ce Amurka suna tare da iyalan Sarauniyar da kuma mutanen Birtaniya.

Shugaban Faransa, Emmanuel Macron ya bayyana marigayiyar a matsayin kawar Faransa, wadda ta bada gudumawa wajen hadin kai da kuma ci gaban Birtaniya a shekaru 70 da tayi tana mulki.

Firaministan Italiya, Mario Draghi ya bayyana marigayiyar a matsayin wadda ta zama alamar Birtaniya da kasashe renon Ingila wajen samar da daidaito da kuma basira.

Sauran shugabannin da suka aike da sakon ta’aziya sun hada da Firaministan India, Narendra Modi da takwaransa na Canada Justin Truduea da shugaban Ireland, Michael Higgins da Firaministan Netherlands, Mark Rutte da shugabar kungiyar Turai Ursula von der Leyen da Sakatare Janar na kungiyar NATO Jesn Stoltenberg.

Sai kuma tsoffin shugabannin kasar Amurka Donald Trump da Barack Obama da kuma tsohon shugaban Faransa Nicolas Sarkozy da suma suka aike da sakon ta'aziya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.