Isa ga babban shafi

Ambaliyar ruwa ta kashe mutane 79 a Brazil

Akalla mutane 79 ne suka rasa rayukansu a Brazil sakamakon ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka shatata, lamarin da ya yi sanadiyar bacewar gomman mutane kamar yadda hukumomin kasar suka tabbatar.

Har yanzu akwai mutanen da ba a gano su bayan sun bace a sanadiyar ambaliyar ruwan.
Har yanzu akwai mutanen da ba a gano su bayan sun bace a sanadiyar ambaliyar ruwan. © AP - Marlon Costa
Talla

Yanzu haka masu aikin ceto na ci gaba da neman sauran mutane da watakila ke da nisan kwana, yayin da aka bayyana wannan ibtila’in na ambaliyar ruwa a matsayin mafi muni da kasaar ta gani a baya-bayan nan.

Adadin mutanen da lamarin ya rutsa da su ya karu sosai a karshen mako da suka hada da wadanda zabtarewar laka ta share su  bayan ruwan saman ya haddasa tunbatsar wasu koguna a kasar.

Kawo yanzu, hukumomin kasar ba su bada cikakken bayani ba game da ainihin mutane da suka bace a sanadiyar musibar, amma da farko jami’an tsaron farin kaya na kasar sun ce, mutane 56 ne suka bace, yayin da kusan dubu 4 suka rasa gidajensu.

Gwamnan Pernambuco, Paulo Camara ya bayyana cewa, za a ci gaba da aikin ceto har sai an gano sauran mutanen da suka yi batan-dabo.

A bangare guda, masu hasashen yanayi sun ce, da yiwuwar a ci gaba da zabga ruwan sama kar da bakin kwaraya a wannan rana ta Litinin a kasar ta Brazil.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.