Isa ga babban shafi
Taron Majalisar Dinkin Duniya

Babu wata fa'ida dangane da baiwa Taliban damar magana a zauren MDD - Jamus

Kasar Jamus ta ce babu wata fa’ida cikin baiwa kungiyar Taliban damar halartar taron majalisar dinkin duniya karo na 76.

MInistan harkokin wajen Jamus, Heiko Maas.
MInistan harkokin wajen Jamus, Heiko Maas. Michael Sohn POOL/AFP
Talla

Ministan harkokin wajen kasar ta Jamus Heiko Maas ya ce abin takaici ne ma yadda aka baiwa Taliban damar magana har ma ta bukaci a ba ta damar gabatar da jawabi.

A cewar Maas, duk wani jawabi da Taliban din za ta yi wa jama’a bashi da wata Fa’ida, matukar ba za su yi biyayya ga dokokin kasa da kasa da kuma cika alkawurran da suka dauka.

A cewar Ministan, hatta halartar Taron da Taliban din ta yi ma bashi da wani muhimmanci, a don haka bai kamata a basu damar yin wani jawabi ba, har sai an ga sun fara daukar matakai ba wai zancen fatar baki ba.

Idan dai za’a iya tunawa Taliban ta fara fuskantar matsin lamba daga kasashen duniya tun lokacin da ta sake karbe iko da gwamnatin kasar a cikin watan Agustan da ya gabata.

Wannan ta sa kasashen duniya ke bayyana fargaba a game da makomar hakkin dan adam a kasar da kuma yadda Taliban din ta fara karya alkawurran da ta dauka na kare hakkin mata.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.