Taliban ta bayyana yada za ta gudanar da mulkin Afghanistan
Kungiyar Taliban ta gudanar da taron manema labarai na farko, tun bayan kwace iko da ta yi da Afghanistan, inda ta yi shelar kawo karshen yakin da kasar ta shafe shekaru 20 a cikinsa, tare da sanar da yiwa dukkanin masu adawa da ita afuwa.
Wallafawa ranar:
Yayin taron manema labaran, kakakin kungiyar ta Taliban Zabihulla Mujahid ya yi alkawarin baiwa mata damar gudanar da ayyuka bisa tsarin addinin Musulunci, sabanin yadda matan suka kasance a karkashin kungiyar a fiye da shekaru 20 da suka gabata.
Mujahid ya kara da cewa nan gaba kadan za su kafa sabuwar gwamnati, sai dai bai yi cikakken bayan kan yadda za ta kasance ba, illa kawai za a baiwa dukkanin bangarori dama.
Jim kadan bayan, taron manema labaran na Taliban ne kuma mataimakin shugaban kungiyar Mullah Abdul Ghani Baradar wanda ya taka rawa wajen kafuwarta ya isa Kandahar, tsohon babban birnin Afghanistan a zangon farko na mulkin ‘yan Taliban fiye da shekaru 20 baya.
Yayin tsokaci kan sauyin da aka samu a Afghanistan, jim kadan bayan taron gaggawa na ministocin waje na kasashen EU, babban jami’in kula da harkokin waje na kungiyar Tarayyar Turan Josep Borell ya ce dole su tattauna da kungiyar Taliban da a yanzu ke rike da madafun iko, la’akari da nasarar da suka samu, bayan rushewar gwamnatin da kasashen yamma ke marawa baya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu