Isa ga babban shafi
Ecuador

Yan takara biyu ne zasu kara a zaben Ecuador zagaye na biyu

A jiya asabar ne hukumar zaben Ecuador ta fitar da sakamakon zaben  shugabancin kasar ,inda ta ayana cewa dan takara Andres Arauz zai kara da tsohon ma’aikacin banki Guillermo Lasso a zagaye na biyu da zai gudana ranar 11 ga watan Afrilu na shekarar bana.

Wasu daga cikin ma'aikata. a hukumar zaben kasar Ecuador
Wasu daga cikin ma'aikata. a hukumar zaben kasar Ecuador REUTERS - SANTIAGO ARCOS
Talla

Andres Arauz matashi mai shekaru 36  magadin tsohon Shugaban kasar Rafael Correa da ke rayuwa a Belgium tun a shekara ta 2017, ya samu kusan kashi 32 da digo 72 cikin dari na kuri’u,abokin takarrar sa  Lasso ya kuma samu kashi 19 da digo 74 cikin dari.

Tsohon Shugaban kasar Ecuador Rafael Correa
Tsohon Shugaban kasar Ecuador Rafael Correa AFP/Archivos

Tawagar yan sa ido a karkashin kungiyar kasashen yankin Amurka OEA ta yaba matuka ganin yada aka tafiyar da wannan zabe,inda akala mutane  milyan 13 da dubu dari daya suka kada kuri’u su domin kawo karshen shugabancin Lenin Moreno,wanda  jama’ar kasar suka nuna kyama a kan sat un bayan da ya kama karagar mulkin wannan kasa.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.