Isa ga babban shafi
Duniya

Mutane miliyan 50 sun rasa gidajensu dalilin tashe-tashen hankula da bala'o'i

Wani Bincike ya nuna cewar tashin hankali tare da nau’o’in bala’in da aka fuskanta a duniya sun yi sanadiyar raba mutane sama da miliyan 33 da muhallansu a shekarar 2019 da ta gabata, abinda ya jefa su cikin hadarin kamuwa da cutar coronavirus.

Wasu daga cikin miliyoyin 'yan kasar Syria dake gudun hijira a sansanonin wucin gadi, bayanda yaki ya raba da muhallansu.
Wasu daga cikin miliyoyin 'yan kasar Syria dake gudun hijira a sansanonin wucin gadi, bayanda yaki ya raba da muhallansu. AP
Talla

Rahoton da kungiyar dake sa ido kan mutanen da suka bar matsugunan su da kuma kungiyar kula da ‘yan gudun hijira ta kasar Norway suka wallafa, ya bayyana cewar sabbin alkalumman da aka samu ya kawo jimillar adadin mutanen da suka rasa matsugunan su zuwa miliyan 50 da dubu 800.

Daraktan kungiyar Alexandra Bilak, tace yanzu haka akwai irin wadannan mutane miliyan 26 da suka tsallaka iyaka suka bar kasashensu domin samun mafaka, kuma a shekarar da ta gabata, an samu irin wadannan mutane miliyan 8 da rabi a kasashe irin su Syria da Jamhuriyar dimokiradiyar congo da Habasha da kuma Sudan ta kudu.

Rahotan yace yanzu haka mutane sama da miliyan 45 suka tsere daga matsugunan su a duniya, cikin su harda kusan miliyan 6 da rabi da suka gudu daga Syria da aka kwashe shekaru 9 ana yaki, yayin da wasu sama da miliyan 5 suka bar gidajen su saboda wasu bala’oi a bara, daga cikin miliyan 25 da suka bar gidajen su bara.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.