Isa ga babban shafi
Coronavirus-Afrika

Coronavirus ta kusan kama 'yan Afrika miliyan 10-WHO

Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta yi hasashen cewa, za a iya samun karuwar mutane milyan 10 sabbin kamuwa da cutar coronavirus a nahiyar Afrika nan da watanni 3 zuwa 6 masu zuwa duk da kasasncewar nahiyar  mafi karancin masu dauke da cutar a yanzu.

Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi hasashen cewa, nan da 'yan watanni coronavirus za ta kama 'yan Afrika a kalla miliyan 10
Hukumar Lafiya ta Duniya ta yi hasashen cewa, nan da 'yan watanni coronavirus za ta kama 'yan Afrika a kalla miliyan 10 REUTERS/Zohra Bensemra
Talla

Hasashen WHO na zuwa ne duk da matakan da gwamnatocin kasashen nahiyar ke dauka na killace jama'a a gida don dakile yaduwar cutar.

Sai dai Michael Yao, shugaban Sashen Agajin Gaggawa na WHO, reshen Afrika ya ce, ba lallai hasashen hukumar ya iya zama gaskiya ba, kamar dai hasashen da ta yi lokacin annobar Ebola na yiwuwar mutuwar miliyoyin jama'a amma kuma hakan bai tabbata ba, saboda matakan kariyar da jama'a suka dauka.

Acewar Michael Yao, matakan lafiyar da ake dauka da ma damarar da jama'a suka daura na hana yaduwar cutar matukar suka ci gaba da tabbata ko shakka babu, hasashen hukumar ba zai tabbata ba.

Kawo yanzu dai fiye da mutum dubu 17 aka tabbatar sun kamu da cutar ta corona a nahiyar Afrika ciki har da 900 da suka mutu, adadin da ke nuna nahiyar a matsayin mafi karancin masu dauke da cutar.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.