Dakarun Amurka sun kashe Qassim al-Rimi
Shugaban Amurka Donald Trump ya tabbatar da kisan shugaban kungiyar Al-Qaeda a Yemen, kwanaki bayan kungiyar ta dau alhakin gagarumin harin bindiga da aka kai wani sansanin sojin ruwan Amurkan.
Wallafawa ranar:
Trump kamar dai yada ya dau alkawali a lokutan zabe ya ce Amurka ba za ta kawar da idanu yan ta'adda na ci gaba da rusa kokarin kasashe don tabbatar da zaman lafiya a yankunan su,Shugaba Trump ya bayyana cewa kasar sa Amurka ta kaddamar da wani hari kan ‘yan ta’adda a Yemen, kuma tayi nasarar kashe Qassim al-Rimi, mutumin da ya kafa kungiyar Al-Qaeda a yankin.
A ranar Lahadi kungiyar ta dau alhakin harin da aka kai sansanin sojin ruwan Amurka da ke Pensacola a jihar Florida a ranar 6 ga watan Disamba, inda aka kashe wani sojin Saudiyya da wasu sojin ruwan Amurka 3.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu