Isa ga babban shafi
Yemen

Saudiya na shirin sakin mayakan Huthi 200

Rundunar hadaka da Saudiya ke jagoranta a Yemen, ta ce, za ta saki mayakan Huthi 200 da take tsare da su, a daidai lokacin da aka kara kaimi wajen kawo karshen rikicin da ya daidaita kasar mai fama da talauci.

Wasu daga cikin mayakan Huthi na Yemen
Wasu daga cikin mayakan Huthi na Yemen ©REUTERS/Khaled Abdullah
Talla

Mai magana da yawun rundunar hadakar, Turki al-Maliki ya ce, za su bai wa hatta marasa lafiya damar tashi daga filin jiragen sama na birnin Sana’a domin su je su nemi magani , duk da cewa, tun shekarar 2016 aka hana jiragen fasinjoji jigila a wannan filin jiragen saman.

Tuni daya daga cikin jagororin siyasar mayakan Huthi, Mohammed Ali al-Huthi, ya yi lale marhabin da matakin da rundunar hadakar ta dauka, sannan kuma ya bukaci kawo karshen azabtar da mayakansu da ke tsare a yanzu haka.

Matakin dai na zuwa ne a daidai lokacin da mayakan Huthi suka sassauta kaddamar da hare-hare kan Saudiya, yayin da kuma wani babban jami’n gwamnati a birnin Riyadh ya ce, Masauratar kasar ta samar da wata ‘budaddiyar hanyar ganawa’ tsakaninta da ‘yan twayen.

Jami’in ya bayyana cewa suna goyon bayan zaman lafiya a Yemen, yana mai cewa, ko dan ba su rufe kofofinsu ga ‘yan Hurthi ba.

A ranar Jum’ar da ta gabata ne, Jakadan Majalisar Dinkin Duniya, Martin Griffiths ya ce, hare-haren da rundunar hadakar ke kaddamar sun ragu matuka a cikin makwanni biyu da suka gabata, abin da ke nuna cewa, ana samun sauyi a Yemen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.